COMA' PROJECT – Telegram
COMA' PROJECT
143 subscribers
579 photos
22 videos
1 file
54 links
Download Telegram
Ƙungiyar malaman jami'o'i ta ƙasa wato ASUU ta shiga tattaunawa da wakilan gwamnatin tarayya domin magance yunƙurin ƙungiyar na tsunduma yajin aikin sai baba ta gani da suke shirin yi.
Za mu kuɓutar da duk kanin ƴan Najeriyar da ke hannun masu garkuwa da mutane.
Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusif, ya bada umarnin rufe duk wasu asusun hukumomin gwamnatin jihar nan da sa'o'i 48 domin samar da asusun bai ɗaya.
Media is too big
VIEW IN TELEGRAM
Jama'a ga saƙo daga bakin ƴar jarida Kadaria Ahmed
Media is too big
VIEW IN TELEGRAM
Ƙasar Nijar da Ƙasar Najeriya sunyi zama a yau a ƙasar Nijar inda suka sanar da kawo karshen zaman doya da man ja da aka kwashe sama da shekara ɗaya ana yi tun lokacin da sojojin Nijar suka kifar da gwamnatin tsohon shugaban ƙasar Nijar Bazom ranar 26 ga watan Yulin 2023. Babban hafsan hafsoshin Najeriya Janar Musa Christopher yayi jawabi ga ƴan jaridu bayan gama tattaunawar ƙasashen guda biyu.
Yadda aka yi hada-hadar kudaden waje zuwa Naira a kasuwar sauyin kuɗi ta Wapa da ke jihar Kano.
#premierradio #premierkano #premierradiong
"If we win Edo, we will be getting an additional state for the party. It will be 21 states out of 36"
Gwamnatin Bola Tinubu za ta bai wa asibitocin gwamnati a Najeriya tallafin kashi 50 cikin 100 na kuɗin wutar lantarki
Wani rahoto da cibiyar tsaro ta SB Morgen Intel ta fitar ya nuna cewa cikin shekara ɗaya an yi garkuwa da mutane 7,568 a hare-hare 1,130 da aka kai a faɗin Najeriya.

Rahotan ya ce an biya Naira biliyan 1.048 a matsayin kudin fansar mutanen da aka sace a ƙasar.
UEFA ta karrama Cristiano Ronaldo a matsayin ɗan wasan da ya fi cin ƙwallo a tarihin Gasar Zakarun Nahiyar Turai ta Champions League.
Media is too big
VIEW IN TELEGRAM
Vice President Harris reiterated her support for a "two-state solution" between Israel and Gaza on Thursday in an exclusive interview with CNN's Dana Bash.
Mazauna ƙauyen matusgi a Talatar Mafara dake jihar Zamfara sun hallaka ƴan bindiga har mutum 37 lokacin da suke ƙoƙarin yin garkuwa da mutane a ƙauyen.
Media is too big
VIEW IN TELEGRAM
SIYAR DA FILAYEN MAKARANTUN GWAMNATI A JIHAR KANO.

Kamar yadda kowa ya sani gwamnatin baya wato ta Dr. Abdullahi Umar GANDUJE ta yanka filayen a makarantun gwamnati wanda hakan ya jawo cece kuce a faɗin jihar da kuma ƙasa baki ɗaya wanda a wannan lokaci ƴan Kwankwasiyya sun ɗauki alwashin madamar suka samu gwamnati sai sunyi "rebuked" na filayen.

Bayan APC sun faɗi zaɓe Kwankwasiyya sunyi nasara sai suka cika alkawarin da suka ɗauka akan filayen da gwamnatin Ganduje ta yayyanka, sai kuma yanzu ga wata sabuwa ana ZARGIN gwamnatin Kwankwasiyya da cigaba da inda gwamnatin Ganduje ta tsaya akan yankan filayen jikin makarantun gwamnati.

Shin wai yanzu me hakan yake nufi?